in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsarin kasar Sin na hulda da kasashen waje na amfanawa sauran sassan duniya
2018-03-17 10:41:54 cri
Jaridar Le Renouveau ta kasar Burundi ta bayyana tsarin kasar Sin na hulda da kasashen waje a matsayin wanda ke amfanawa sauran sassan duniya.

Jaridar ta ruwaito a jiya cewa, kokarin da kasar Sin ta yi, ya yi kyakkyawan tasiri kan samar da sauyi a zirin Korea.

Har ila yau, ta ce duniya baki daya, musammam nahiyar Afrika, na amfana sosai daga hadin gwiwa da kasar Sin dake kasancewa bisa gaskiya da adalci da daidaito da moriyar juna da aminci da kawance da kuma mara baya ga juna.

Jaridar ta kara da bayyana hadin gwiwa da kasar Sin a matsayin muhimmiya, wadda ke kara fahimtar juna da bada damar cimma matsaya guda da kuma kaucewa tsoma baki cikin harkokin cikin gida. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China