in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya na kokarin tattara magoya bayan kungiyar Super Eagles domin gasar kwallon kafa da za a yi Rasha
2018-03-16 09:30:03 cri
Gwamnatin Nijeriya ta ce za ta tattara magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta super Eagles a fadin duniya domin gasar cin kofin duniya ta FIFA ta bana.

Shugaban hukumar raya al'adu ta kasar Olusegun Runsewa ne ya bayyana haka a jiya, inda ya ce dukkan magoya bayan kungiyar za su sanya tufafi daban-daban na gargajiya tare da daga tutar kasar a ranekun da Super Eagles din za su buga wasa.

Ya ce nan bada dadewa ba za bude shafin website ta yadda magoya bayan za su shiga.

Ya kara da cewa wannan al'ada ce da aka saba yi a sauran kasashen duniya, inda ya ce ba za a bar Nijeriya a baya ba.

Kasar Rasha ce za ta karbi bakuncin gasar cin kofin duniya ta FIFA ta bana da za a yi tsakanin ranekun 14 ga watan Yuni da 15 ga watan Yuli, inda Nijeriya ta fada rukuni na D tare da kasashen Argentina da Crotia da Iceland. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China