in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ci gaba da kokarin ganin an warware batun nukiliyar zirin Koriya
2018-03-13 18:58:20 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yau Talata yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing cewa, kasar Sin za ta ci gaba da taka rawarta wajen ganin an warware batun nukiliyar zirin Koriya, karfafa gwiwar sassa daban daban da su tattauna a tsakanin juna domin samun sakamako mai kyau, a kokarin tabbatar da samun zaman lafiya, kwanciyar hankali da ganin an kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya.

A jiya ne, Chung Eui-yong, wakilin musamman na shugaban kasar Koriya ta Kudu ya ziyarci kasar Sin, inda ya tattauna da bangaren Sin dangane da ziyarar da ya kai a kasashen Koriya ta Arewa da Amurka. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China