in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta mika ta'aziyya dangane da wadanda suka mutu a hadarin jirgin sama a Nepal
2018-03-13 18:56:28 cri

Yau Talata ne Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing cewa, kasar Sin ta yi bakin ciki sosai da samun labarin rasuwa da jikkatar wasu mutane sanadiyar hadarin jirgin sama a kasar Nepal, tare da mika ta'aziyya dangane da wadanda suka rasa rayukansu a hadarin.

A jiya ne, wani jirgin saman fasinja dauke da mutane 71 da ya tashi daga birnin Dhaka na kasar Bangladesh zuwa kasar Nepal ya wuce titin saukarsa inda ya fadi ya kuma kama da wuta, inda mutane 49 suka mutu, kana an kai mutane 22 da suka ji rauni zuwa asibiti. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China