in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 49 sun mutu a hadarin faduwar jirgin sama a kasar Nepal
2018-03-13 14:11:06 cri
A jiya ne, wani jirgin saman fasinja da ya tashi daga birnin Dhaka na kasar Bangladesh zuwa kasar Nepal ya wuce titin saukarsa inda ya fadi ya kuma kama da wuta.

Rahotanni da kafofin watsa labaru na kasar Nepal suka bayar, na cewa mutane 49 ne suka mutu,kana an kai mutane 22 da suka ji rauni zuwa asibiti, wasu daga cikinsu sun ji munanan raunuka

Jirgin saman da ya fadi samfurin BS-211 mai daukar mutane 78 mallakin kamfanin US-Bangla Airline ne. Jirgin dai yana dauke da fasinjoji 67 da kuma ma'aikata 4, ciki har da mata 28 da yara 2 'yan kasar Bangladesh. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China