in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 16 sanadiyyar wasu hare-hare a kasar
2018-03-12 10:50:34 cri
Rundunar 'yan sandan jihar Plateau dake arewa maso tsakiyar Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar mutane 16 tare da jikkatar wasu da dama, sanadiyyar hare-haren da aka kai wasu kauyukan jihar.

Kakakin rundunar 'yan sanda Terna Tyopev, ya shaidawa manema labarai a Jos babban birnin jihar cewa, 'yan sanda sun kama wani makiyayi mai suna Muhammadu Musa Bimini tare da bindiga kirar AK-47 a ranar 8 ga watan nan.

A nasu bangaren, shugabanni a yankunan da al'amarin ya auku sun ce an kashe mutane da yawansu ya kai 25 yayin hare-haren.

Shugabannin sun kuma shaidawa manema labarai cewa har yanzu kwai wasu mutane da ba a gansu ba.

Hare-haren sun auku ne kasa da sa'o'i 24 bayan shugaban kasar Muhammdu Buhari ya kai ziyarar yini daya Jos. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China