in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD ta yi gargadin daukar mataki mai tsauri saboda karuwar gibi a kasafin kudinta
2018-03-12 10:47:40 cri
Hukumar MDD dake bada agajin jin kai ga 'yan gudun hijirar Falasdinu, ta yi gargadin cewa, gibin kasafin kudinta dake kara tabarbrewa zai tilasta mata daukar mataki mai tsauri.

A cewar daraktan sashen ayyukan hukumar a Gaza wato Matthias Schmale, idan kasashe masu bada tallafi ba su bada sabuwar gudunmuwa don tallafawa hukumar gudanar da ayyukanta na kiwon lafiya da samar da ilimi ba, to ayyukanta za su fuskanci barazana ya zuwa watan Mayu.

Jami'in wanda ya soki kasashen duniya game da gazawa wajen warware matsalar 'yan gudun hijirar Falasdinu, ya ce kaso 77 cikin 'yan gudun hijirar Falasdinu miliyan 1 dake karbar tallafin abinci a Gaza, na rayuwa ne kasa da matakin talauci. (Fra'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China