in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakiliyar MDD ta nuna damuwa game da halin da ake ciki a DRC
2018-03-08 09:49:18 cri

Wakiliyar MDD ta bayyana damuwa game da yanayin tabarbarewar al'amurran siyasa da tsaro da yanayin rayuwar bil adama a jamhuriyar demokaradiyyar Congo DRC, duk kuwa da ci gaban da aka samu game da shirye-shiryen gudanar da zabuka a kasar.

Da take jawabi ga kwamitin sulhun MDD, Leila Zerrougui, wakiliyar musamman ta babban sakataren MDD a DRC, ta bayyana cewa, an samu gagarumin ci gaba a 'yan makonnin da suka gabata a shirye shiryen gudanar da zaben shugaban kasar da na 'yan majalisun dokoki, ciki kuwa har da batun kammala aikin rijistar masu zabe.

Sai dai kuma ta yi gargadin cewa, har yanzu akwai wasu manyan kalubaloli da suka dabaibaye kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China