in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yaba da kyakyyawan sakamakon da aka samu bisa ziyarar da tawagar wakilan Koriya ta Kudu ta kai Koriya ta Arewa
2018-03-07 10:22:37 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta yaba da kyakkyawan sakamakon da aka samu dangane da ziyarar da tawagar wakilan shugaban kasar Koriya ta Kudu ta kai wa kasar Koriya ta Arewa.

Kakakin ma'aikatar Geng Shuang ya bayyana a jiya cewa, kasar Sin na goyon bayan kyautata dangantakar dake tsakanin kasashen biyu a ko da yaushe, kana, tana goyon bayan warware dukkanin sabanin dake tsakaninsu ta hanyar tattaunawa da kuma gaggauta aikin kawar da makaman nukiliya daga yankin Koriya. A cewarsa, Sin na ganin hakan zai dace da moriyar bangarorin da abin ya shafa da kuma biyan bukatun al'ummomin kasashen biyu, sannan, zai tabbatar da kiyaye zaman lafiyar yankin baki daya.

Ya kuma kara da cewa, ana fatan kasashen biyu za su aiwatar da matakan da suka cimma ra'ayi guda a kai yadda ya kamata tare da gaggauta neman sulhu a tsakaninsu. Inda a nata bangaren kasar Sin, za ta bada gudummawa kan batun cikin himma da kwazo. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China