in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta ce za ta yi dukkan mai yuwa wajen ceto 'yan matan sakandare da aka sace
2018-03-07 09:07:15 cri
Ministan tsaron Nijeriya Mansur Dan Ali ya ce dole ne a yi amfani da duk wasu damarmakin dake akwai ta hanyar amfani da tsarin tauraron dan Adam mai sanya ido tare da samun goyon bayan al'umma, wajen ceto 'yan matan sakandaren Dapchi da aka sace.

Da yake jawabi a wani taro kan tsaro da ya gudana jiya a Abuja babban birnin kasar, Mansur Dan Ali, ya ce dole ne a yi dukkan mai yuwa dan kare sake aukuwar lamarin a nan gaba.

A ranar 19 ga watan Fabrerun da ya gabata, wasu da ake zargin mayakan Boko Haram ne, suka sace 'yan mata dalibai 110 na kwalejin kimiyya da fasaha ta Dapchin jihar Yobe dake yankin arewa maso gabashin kasar.

Al'amarin na zuwa ne shekaru 4, bayan 'yan wannan kungiya sun yi wa sakandaren 'yan mata ta Chibok tsinke, inda suka sace fiye da 'yan mata 200

Har ila yau, Ministan ya ce akwai bukatar samar da ingantacciyar hanyar magance barazanar kutsen intanet. Saboda a cewarsa, galibin kungiyoyin 'yan ta'adda sun koma amfani da kafar intanet wajen jan hankali da daukar sabbin mambobi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China