in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya: Nahiyar Afrika na fuskantar matsalar ba da ilmi
2018-03-06 09:39:20 cri
Wani rahoton binicike da bankin duniya ya fitar a jiya Litinin a Tanzaniya ya nuna cewa, yawaitar matsalar ba da ilmi da ake fuskanta a Afrika yana matukar gurgunta cigaban tattalin arzikin nahiyar da tagayyara yanayin zaman rayuwar al'umma.

Rahoton binciken wanda aka fitar a Dar es Salaam, birnin kasuwancin kasar Tanzania ya ayyana cewa, matakin ilmi a fadin nahiyar yana kara fuskantar koma-baya.

Rahoton ya ce, ko da yake an dan samu cigaba ta fuskar shigar da yara a makarantun firamare da karamar sakandare, to sai dai duk da haka, akwai yara kanana sama da miliyan 50 wadanda ba su zuwa makarantun, kuma mafi yawan wadanda suka yi dacen kammala karatunsu ba su samun kwarewar da za ta ba su damar samun kyakkyawar makoma a rayuwarsu ta nan gaba.

A cewar rahoton binciken, gwamnatocin kasashen Afrika suna kashe dalar Amurka 204 ne kacal a kan ko wane dalibin makarantun firamare, a bisa shekarar 2014, kasa da rabin kason da ake kashewa daliban firamaren a kudancin Asiya, yankin wanda shi ne na biyu mafi karancin kashe kudaden ga dalibai. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China