in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya ya yi tir da harin da Boko Haram ta kai wa jami'an bada agaji
2018-03-03 13:59:46 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya tir da kakkausar murya kan harin da ake zargin kungiyar Boko Haram da kai wa garin Rann dake arewa maso gabashin kasar, wanda ya yi sanadin mutuwar jami'an bada agaji 3 da yammacin ranar Alhamis.

Cikin wata sanarwa, Muhammadu Buhari ya ce harin ya nuna cewa 'yan ta'addan ba su da imani bare tausayi.

Shugaba Buhari ya jajantawa MDD da sauran hukumomin agaji dake aiki a Rann, inda ya ce harin na mastorata zai kara zaburar da kudurin gwamnati ne na kawo karshen kungiyar Boko Haram cikin kankanin lokaci.

A jiya Juma'a ne MDD ta tabbatar da kisan jami'an 3, inda ta ce akwai wani ma da ake fargabar ya mutu da kuma wani da aka sace yayin harin, har ila yau, wata jami'ar kiwon lafiya ta samu rauni.

A cewar kakakin MDD a Nijeriya Samantha Newport, dukkan jami'an da harin ya rutsa da su 'yan asalin kasar ne. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China