in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Boko Haram ta tabbatar da sace 'yan mata 110 na sakandaren Dapchi da suka bata
2018-03-03 13:59:02 cri
Wani tsagi na kungiyar Boko Haram, ya tabbatar da cewa ya na rike da 'yan matan nan 110 da suka bata a garin Dapchin jihar Yobe dake yankin arewa maso gabashin Nijeriya.

Babbar mai shiga tsakanin rundunar sojin Nijeriya da kungiyar ta Boko Haram Aisha Alkali wakil ce ta bayyana haka a jiya Juma'a.

Aisha Alkali wadda Lauya ce kuma fitaciyar mai rajin kare hakkin dan Adam dake zaune a yankin na arewa maso gabashin kasar, ta ce tsagin Abu Musab Al-Barnawi ya tuntube ta a ranar Alhamis da ta gabata, inda ya tabbatar mata cewa ya na rike da 'yan matan. A cewarta, 'yan matan suna nan cikin koshin lafiya.

Aisha Alkali da ake wa lakabi da 'mama Boko Haram' a Nijeriya, ta shaidawa wakilin kamfanin dillancin labarai na kasar cewa, shgugaban tsagin wato Al-Barnawi, ya yi alkawarin ba zai illata ko kashe 'yan matan ba.

A farkon wannan makon ne fitattaciyar lauyar mai rajin kare hakkin dan Adam ta gano wadanda suka sace 'yan matan, inda ta roki su sake su.

Ta ce tsagin kungiyar ya kira ta ne ta la'akari da rokon da ta yi musu.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China