in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 14 sun bace sakamakon nitsewar jiragen ruwa guda biyu a Congo(Kinshasa)
2018-03-01 11:10:42 cri
Jiya Laraba, ma'aikatar harkokin cikin gidan Congo(Kinshasa) ta fidda sanarwa cewa, a daren ranar 26 ga wata, jiragen ruwa guda biyu sun nitse a kogin Congo dake yammacin kasar, hadarin da ya haddasa bacewar mutane 14.

Haka kuma, an ce, a daren ranar 26 ga wata, jiragen ruwan biyu sun tashi daga lardin Mai-Ndombe, sa'an nan sun nitse a kogin Congo sakamakon kadawar iska mai karfi da mamakon ruwan sama.

Bisa kididdigar da aka yi, an ce, mutane 108 sun tsira daga hadarin, yayin da mutane 14 suka bace. Haka kuma, wani jami'in ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ya nuna cewa, babu tabbas ko wadanda suka bace din za su tsira daga wannan hadari.

Akwai albarkatun tabkuna da koguna cikin kasar ta Congo(Kinshasa), kuma mazauna wurin su kan yi tafiye-tafiye cikin jiragen ruwa, amma, an sha fama da hadarurrukan nitsewar jiragen ruwa a kasar sakamakon lalacewar jiragen ruwa ko kuma daukar mutane fiye da kima. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China