Wani jami'in rundunar ya bayyana cewa, dakarun sun kai hari a gaban sansanin rundunar dake yankin karkarar birnin Quetta, an kuma yi musayar wuta mai tsanani a wurin.
Bayan aukuwar harin, wasu rundunonin sojojin tsaro da masu ba da agaji sun isa wurin, inda suka toshe wurin da harin ya auku, sa'an nan suka fara neman wadanda suka taimakawa dakarun da suka kai harin. (Maryam)