in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guinea Bissau na son kara musayar ra'ayi da Tunisia
2018-02-28 13:38:07 cri
Teodoro Obiang, shugaban kasar Guinea Bissau dake ziyarar aiki a kasar Tunisia, ya furta a jiya Talata cewa, kasarsa na son kara musayar ra'ayi da Tunisia, bisa ayyukan kula da makaurata, da rage talauci, da tsaro, da cigaban kasa da dai makamantansu, ta yadda za a samu damar daga matsayin nahiyar Afirka a idanun duniya.

Duk a jiya Talata, Beji Essebsi, shugaban kasar Tunisia, ya gana da shugaba Obiang a fadar shugabancinsa, inda suka ganewa idanunsu yadda aka kulla yarjeniyoyi da dama tsakanin bangarorin 2 masu alaka da ayyukan lafiya, da yawon shakatawa, da aikin noma, da dai sauransu. A cewar shugaba Obiang na kasar Guinea Bissau, ziyarar da ya kai Tunisia a wannan karo na tare da dimbin nasarori da ma'anar tarihi, saboda haka kasarsa na sa ran ganin kara yin hadin gwiwa tare da Tunisia. Ya kara da cewa, za a baiwa 'yan kasar Tunisia damar shiga Guinea Bissau cikin 'yanci ba tare da bukatar neman samun izinin shiga ba, kana za a kafa ofishin jakadancin kasar Guinea Bissau a hedkwatar kasar Tunisia.

A nashi bangaren, shugaban kasar Tunisia, Beji Essebsi, ya nuna maraba da matakan da kasar Guinea Bissau za ta dauka, ya ce Tunisia na son raba fasahohin da ta samu a fannonin siyasa da yawon shakatawa ga kasar Guinea Bissau, sa'an nan za a yi kokarin neman kara kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China