in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gamayyar kasa da kasa sun mai da hankali kan niyyar kasar Sin ta gyaran fuskar tsarin mulki
2018-02-28 13:10:03 cri
Kwanakin baya, kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya bada shawara ga zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, inda ya bukaci a gyara wasu bayanan dake cikin kundin tsarin mulkin kasar ta Sin. Sai dai wannan batu ya janyo hankalin kafofin watsa labaru na kasashen waje da dama, wadanda suka ce shawara ce mai ma'ana matuka, musamman ma fannin taimakawa jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ladabtar da 'ya'yanta, da kyautata dabarunta wajen mulkin kasa.

Kamar yadda kamfanin dillancin labaru na Reuters na kasar Birtaniya ya bada labarin cewa, shawarar da kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin ya gabatar ta nuna niyyar yin amfani da tsarin mulki wajen gudanar da mulki, inda aka mai da aiwatar da tsarin mulki abu mafi muhimmanci cikin yunkurin kasar na gudanar da harkokin mulki bisa doka.

A nasa bangare, kamfanin dillancin labaru na Tars na kasar Rasha ya ce, ana neman gyaran tsarin mulkin kasar Sin ne don baiwa kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin damar kara taka rawa a fannonin hadin kan mambobin jam'iyyar, da al'ummomin kasar daban daban, da neman samun walwala a kasar daga dukkan fannoni.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China