in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gabatar da bukatar yin gyaran fuska a kundin tsarin mulkin Sin
2018-02-26 09:36:56 cri
A ranar Lahadi kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin (CPC), ya sanar da jama'a game da bukatarsa ta neman yin gyaran fuska a kudin tsarin mulkin kasar Sin.

Bukatar, an mika ta ne ga zaunannen kwamitin wakilan jama'ar kasar Sin, kuma an gabatar da ita bisa ga sabon tsarin gurguzu wanda ya dace da halayyar musamman ta kasar Sin a sabon karni.

Kwamitin tsakiyar ya gabatar da bukatar yin gyaran fuska ga kuduri dokar nan wanda ta nuna "Wa'adin shugaban kasa da mataimakinsa a kasar Sin daidai yake da majalisar wakilan jama'ar kasa, kuma ba za su shafe sama da wa'adin mulki biyu ba" zuwa "Wa'adin shugaban kasa da mataimakinsa a tsarin shugabancin kasar Sin iri daya ne da na majalisar wakilan jama'ar kasa."

Kwamitin tsakiyar na jam'iyyar ta CPC ya mika bukatar sanya kwamishinoni masu gafaka a matsayin wani sabon bangare cikin kundin tsarin mulkin kasar.

A cewar bukatar, za'a sanya kwamishinoni masu gafakar cikin jerin sunayen jami'an gudanar da mulki, da jami'an shari'a, a matsayin wani bangare na shugabancin kasa, dukkansu majalisar wakilan jama'a ne za su samar da su da kuma duba alhakin dake wuyansu da yadda aikinsu ke gudana. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China