in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gidana talabijin na Rwanda ya gabatar da shirin girke girken abincin Sinawa
2018-02-25 12:35:28 cri
Tashar talabijin mai watsa shirye shirye mallakin kasar Rwanda (RTV), a ranar Asabar ta nuna wani shirin talabijin dake nuna nau'ikan abincin Sinawa ga al'ummar kasar ta Rwanda.

An tsara gabatar da zagaye na gabata na shirin abincin Sinawan a cikin shirin girke girke na RTV mai take Foodtube.

An dai nuna shirin abincin sinawan ne a ofishin jakadancin kasar Sin dake Kigali, babban birnin kasar Rwandan.

Jakadan kasar Sin a Rwanda Rao Hongwei, ya bayyana muhimmancin dake tattare da shirin girke girken sinawan, inda yace hakan zai kara bayyana al'adun sinawa da kuma dalilan da suka sanya abincin sinawa ke kara samun karbuwa a duk fadin duniya.

Tao Yukun, mai yin girki a ofishin jakadancin kasar Sin, ya dafa nau'ikan abincin sinawa masu yawan gaske domin nunawa a cikin shirin.

Munyangeyo, wani mazaunin kasar Rwandan ya bayyana cewa, masu kallon shirin talabijin na RTV ne suka bukaci a gabatar musu da shiri kan nau'ikan abincin sinawa. Akwai shagunan dake sayar da abincin sinawa masu yawa a Kigali, kuma mutane suna son a koyar dasu yadda ake girka abincin sinawan domin suma su dafa a gidajensu, in ji shi.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China