in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rwanda ta zama jagorar kasashen gabashin Afrika kan batun yaki da rashawa
2018-02-23 10:42:52 cri
Kasar Rwanda ta cigaba da rike matsayinta na kasa ta 3 dake sahun gaba wajen yaki da rashawa a Afrika kuma ta kasance kasar data samu matsayi na daya a gabashin Afrika, kamar yadda alkaluman hukumar dake bibiyar al'amurran rashawa na kasa da kasa na shekarar 2017 ya nuna.

Daga cikin kasashen duniya 180, Rwanda ta samu matsayi na 48 cikin kasashen dake da karancin aikata rashawa a duniya, inda ta samu cigaba daga matsayin kasa ta 50 a shekarar 2016, kamar yadda rahoton da aka fitar a Kigali babban birnin kasar ta Rwandanya tabbatar. Ita ma kasar Tanzania ta tashi daga matsayin kasa ta 106 a shekarar 2016 inda ta koma kasa ta 103 a shekarar 2017, a cewar rahoton.

Uganda ta cigaba da rike matsayinta na kasa ta 151 a shekarar 2016, yayin da kasar Burundi ta samu hawa matsayi na 157 bayan ta dan samu cigaba a bangarori biyu idan aka kwatanta da shekarun baya.

Kenya kuwa ta sauka kasa da maki biyu inda ta hau matsayi na kasa ta 143.

Botswana ce kasa ta farko a nahiyar Africa, inda ta samu matsayi na 34 a duniya baki daya, yayin da Seychelles a Afrika ta samu matsayi na 36 a duniya, kamar yadda rahoton ya nuna.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China