in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD: Jamhuriyar Afrika ta tsakiya da rikici ya daidaita na bukatar tallafi
2018-02-23 10:31:14 cri
Mataimakiyar shugaban shirin kai daukin gaggawa na MDD Ursula Mueller, ta bukaci al'ummomin duniya su bada tallafin jin kai ga Jamhuriyar Afrika ta tsakiya dake fama da rikici, inda kusan rabin al'ummar kasar ke bukatar taimako.

Ursula Mueller ta yi kiran ne jiya a birnin Bangui, bayan kammala ziyarar yini 4 da ta kai kasar.

Ta ce Jamhuriyar Afrika ta tsakiya na fuskantar matsalar jin kai, tana mai cewa rikici na ci gaba da yaduwa a kasar, yayin da jama'a ke cikin tsananin bukatar taimako.

Ta kara da cewa fararen hula ne ke ci gaba da fama da radadin rikicin da rashin tsaro.

Rikici tsakanin musulmi 'yan tawayen Seleka da na Anti-Balaka da galibinsu kiristoci ne, ya jefa kasar cikin yakin basasa tun daga shekarar 2013.

Ofishin MDD mai kula da harkokin jin kai ya bayyana kasar a matsayin mai rauni, wadda rikici ya daidaita, kuma take fuskantar kalubalen tattalin arziki da tsare-tsare. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China