in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnaonin Jam'iyya mai mulkin Nijeriya sun tattauna dangane da zabukan 2019
2018-02-23 10:28:12 cri
A jiya da yamma ne ake sa ran Gwamnonin Jam'iyya mai mulkin Nijeriya su gana da shugaban Kasar Muhammadu Buhari dangane da zabukan 2019.

Shugaban kungiyar Gwamnonin Jam'iyyar APC, Rochas Okorocha ne ya bayyana hakan ga manema labarai jiya a Abuja fadar mulkin kasar.

Da farko dai, Gwamnonin sun halarci taron majalisar zartarwa da ya gudana a fadar shugaban kasar karkashin jagorancin Shugaba Muhammdu Buhari.

Wasu majiyoyi daga jam'iyyar sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, makasudin shirya taron shi ne, shawo kan shugaba Buhari game da bukatar ya sake tsayawa takara a shekarar 2019.

Taron na iya zama dori akan wanda aka yi a garin Daura ranar Juma'ar da ta gabata a gidan Shugaban kasar.

Sai dai kafin haka, Gwamnan dai ya ce manufarsu ita ce yi wa shugaban ta'aziyya game da rashin da ya yi na 'yan uwansa biyu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China