in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya ya umarci ministocinsa su gudanar da bincike kan harin da kungiyar Boko Haram ta kai wata Kwalejin 'yan mata
2018-02-22 12:45:08 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya umarci ministocinsa 3 da su gudanar da bincike kan harin da kungiyar Boko Haram ta kai wata kwalejin 'yan mata a farkon makon nan.

Muhammadu Buhari ya bukaci Ministocin da suka hada da na tsaron kasar Mansur Dan Ali da na harkokin waje Geoffrey Onyeama da kuma Ministan yada labarai Lai Mohammed, su ziyarci kauyen Dapchi na jihar Yobe dake arewa maso gabashin kasar, domin tattaro bayanai na ainihi game da harin da aka kai kwalejin fasaha ta 'yan mata mallakar Gwamnati.

A cewar ministan yada labarai na kasar Lai Mohammed, Shugaba Buhari ya kuma umarci sojoji da sauran hukumin tsaro su karbe ragamar kula da kwalejin tare da ceto 'yan matan da suka bata. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China