in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya ta tabbatar da batan dalibai 46 bayan harin da kungiyar Boko haram ta kai wata makaranta
2018-02-22 09:29:34 cri
Gwamnatin Nijeriya ta tabbatar da batan dalibai 46 biyo bayan wani hari da kungiyar Boko Haram ta kai wata makarantar 'yan mata ta jihar Yobe dake arewa maso gabashin kasar a ranar Litinin da ta gabata.

Tun da farko, dalibai 94 ne aka lura sun bata, bayan hukumomin sun gudanar da kidaya a Kwalejin fasaha ta 'yan mata dake yankin Dapchi na jihar Yobe.

Gwamnatin jihar ta ce 'yan mata 8 sun koma a ranar Talata, sannan wasu 20 ma sun koma da safiyar ranar Laraba, bayan sun tsere daga harabar makarantar saboda farmakin da mayakan Boko Haram suka kai musu.

A cewar Kwamishinan ilimi na jihar Mohammed Lamin, Gwamnati na da yakinin sauran 'yan matan za su dawo nan bada dadewa ba.

A nasa bangaren, Kwamishinan 'yan sandan jihar Abdulmalik Sunmonu ya yi watsi da fargabar da ake ko kungiyar Boko Haram ce ta sace 'yan matan, ya na mai cewa rundunar ba za ta iya cewa akwai batun sace 'yan mata yayin harin na ranar Litinin ba.

A cewarsa, ya tambayi shugabar makarantar ko akwai batun sacewa ko kashe wata daliba, sai dai ta amsa da a'a.

A nasa bangaren, wani malamin makarantar ya ce mayakan Boko Haram sun kutsa dakunan kwanan dalibai, al'amarin da ya sanya 'yan matan tsallake katanga inda suka tsere cikin daji. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China