in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon mataimakin gwamnan babban bankin Najeriya ya shiga takarar shugabancin kasar
2018-02-13 09:23:50 cri
A jiya Litinin ne tsohon mataimakin gwamnan babban bankin Najeriya, Kingsley Moghalu ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takarar neman mukamin shugabancin kasar a zaben shekarar 2019. Koda yake bai fadi inuwar jam'iyyar da zai tsaya takara ba.

Moghalu ya shaidawa manema labarai a birnin Legas, cibiyar kasuwancin kasar cewa, lokaci ya yi da masana da kwararru za su karbi ragamar kasar daga hannun 'yan siyasa.

Tsohon ma'aikacin bankin ya ce, ya kamata a raba batun siyasa da kabilanci a Najeriya, kasa mafi yawan al'umma a nahiyar Afirka ta yadda za ta bunkasa ta kuma koma kan matsayinta na jagora a nahiyar.

Ya ce, yadda manyan jam'iyyun siyasun kasar ke rarraba madafun iko tsakanin shiyoyin kasar a baya ba lallai ne a yi amfani da wannan tsari a wannan lokaci ba. Kamata ya yi a halin yanzu a yi amfani da cancanta maimakon kabila ko yankin da mutum ya fito.

Da ya juya ga batun wa'adi na biyu da shugaba Muhammadu Buhari ke nema, Moghalu ya ce, kundin tsarin mulkin ya baiwa shugaban 'yancin neman sake tsayawa takara.

Ya kara da cewa, wajibi ne Najeriya ta sake tunani game da karfafa wanzuwar sassa masu zaman kansu maimakon ci gaba da dagora kan man fetur.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China