in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan kwantar da tarzomar MDD za su janye daga Laberiya
2018-02-07 10:09:14 cri
Tawaga ta musamman da Majalisar Dinkin Duniya ta jibge a kasar Laberiya ta yi wani biki kwanan baya a birnin Monrovia, inda aka sanar da cewa, 'yan sandan kwantar da tarzoma da suke gudanar da ayyukan shimfida zaman lafiya na MDD za su janye daga kasar a karshen watan Maris din.

Bayan bikin, shugaban Laberiya, George Weah, ya gana da 'yan sandan kwantar da tarzoma da kasar Sin ta tura zuwa Laberiya karo na biyar, inda ya gode musu saboda babbar gudummawar da suka bayar ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar ta Laberiya. Weah ya kuma dauki hoto tare da 'yan sandan kasar Sin. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China