in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Namibia ta yi gargadi game da barkewar cutar Maleriya a kasar
2018-02-07 09:50:14 cri
A ranar Talata kasar Namibia ta fitar da wata sanarwar gargadi game da barkewar cutar zazzabin Maleriya ga mazauna da kuma masu tafiye tafiye zuwa yankunan arewacin kasar.

Cikin wata sanarwar da ma'aikatar lafiyar kasar ta fitar ta bayyana cewa, ana samun karuwar wadanda ke kamuwa da cutar ta Maleriya a duk fadin kasar ta kudancin Afrika musamman a 'yan shekarun nan.

Sanarwar ta ce, kasar ta Namibia, ta fuskanci irin wannan matsalar tsakanin shekarar 2015 da 2018 a wasu sassan kasar.

A cewar sanarwar, an samu rahoton bullar cutar maleriya a yankunan Ohangwena, da yammacin Kavango, da Oshikoto, da kuma yankin Zambezi.

Sanarwar ta ce, ma'aikatar lafiyar kasar ta kafa wata tawagar jami'ai don yin feshin magunguna a dukkan yankunan da ake fama da cutar zazzabin maleriyar tsakanin watan Satumba zuwa tsakiyar watan Disambar 2017.

An samu nasarar gudanar da kashi 85 bisa 100 a lokacin aikin feshin, in ji sanarwar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China