Shugaban hukumar Mao Youfeng ya ce, karuwar adadin za ta habaka bukatun al'ummomin kasar Sin, da kuma kyautata ingancin ayyukan samar da kayayyaki, ta yadda za a kyautata ayyukan ba da hidima ga al'ummomin kasar.
Haka kuma, ana ganin cewa, adadin mazauna birane na kasar Sin bai kai matsayi na kasashe masu arziki, wadanda matsayin su ya kai kimanin kashi 80 bisa dari. Lamarin da ya nuna cewa, kasar Sin za ta ci gaba da neman bukasuwa kan wannan aiki, wanda zai ba da taimako wajen ciyar da bunkasuwar tattalin arzikin ta gaba. (Maryam)