in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Birnin Shanghai ya yi kokarin sanya jama'a su kara karanta littafi
2018-02-04 13:41:06 cri
Birnin Shanghai na kasar Sin na daukar wasu sabbin matakai don sanya karin al'umma su fara rungumar dabi'ar karanta littattafai. Yankin Xuhui na birnin ya sanar a kwanakin baya cewa, ana kokarin kafa wani tsarin da ya hada da kungiyoyin jama'a, da wurin shan shayi, da kantunan sayar da littattafai, da dakunan karatu na al'umma, domin baiwa jama'a karin damar karanta littafi.

An fara daukar wannan mataki ne a bara, inda aka yi kokarin gina wasu wurare na musamman da jama'a za su iya karanta littafi a cikinsu, sa'an nan aka sanya jama'a su shiga a dama da su, don yayata dabi'ar karantawa a wadannan wurare na musamman da aka tanada.

Ban da haka, an ba jama'a damar zabar wasu littattafan da suke so a madadin laburare wanda ke da bukatar sayen karin littattafai. Bisa wannan shiri, jama'a za su iya samun littattafai a kantunan sayar da littattafai a kyauta domin su karanta a gida, daga bisani za su iya mayar da littattafan ga dakunan karatu domin ajiye su. Ta wannan mataki, jama'a za su samu damar karanta karin littattafai, yayin da dakunan karatu suka samu littattafan da ake son karantawa. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China