in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta harba tauraron dan Adam na bincike da hasashen girgizar kasa
2018-02-02 20:15:33 cri
A juma'ar nan ne kasar Sin ta harba tauraron dan Adam mai lakabin Zhangheng 1, tauraron da ya kasance irin sa na farko daka iya nazarta, tare da samar da alkaluman hasashen aukuwar girgizar kasa a nan gaba.

An sanya wa tauraron sunansa ne daga sunan wani masani mai suna Zhang Heng, wanda ya rayu yayin daular Han ta gabashi da ta yi mulki tsakanin shekarun 25 zuwa 220. Mr. Zhang Heng dai shi ne masani na farko da ya gudanar da nazari, tare da kirkiro magwajin auna girgizar kasa irin sa na farko a shekara ta 132.

Ana sa ran tauraron Zhangheng 1 zai rika tattara bayanai da suka kai magwajin lamba ta 6 ta girgizar kasa a kasar Sin, da kuma magwajin da ya haura lamba 7 a sauran kasashen duniya, tare da kimanta motsi da ake samu mai nasaba da girgizar kasa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China