in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zhang Dejiang ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Mauritius
2018-02-02 20:04:44 cri
Yau Jumma'a, a nan birnin Beijing, shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Zhang Dejiang ya yi shawarwari tare da takwaransa na kasar Mauritius Mista Shanti Bai Hanoomanjee wanda a yanzu haka ke ziyarar aiki a kasar Sin, inda bangarorin biyu suka rattaba hannu kan takardar fahimtar juna kan hadin-gwiwar hukumomin tsara dokokinsu.

Zhang Dejiang ya bayyana cewa, shugaba Xi Jinping na kasar Sin na maida hankali sosai kan habaka alakar hadin-gwiwa, da karfafa dankon zumunci tare da kasashen Afirka. Sin na fatan Mauritius za ta ci gaba da yin amfani da dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, gami da shawarar ziri daya da hanya daya, domin sa kaimi ga ci gaban huldodinta da kasar Sin, da samar da alfanu ga jama'arsu.

A nasa bangaren Shanti Bai Hanoomanjee ya bayyana cewa, Sin aminiyar arziki ce ta Mauritius, kuma Mauritius na tsayawa kan manufar kasancewar kasar Sin daya tilo a duk fadin duniya. Kana majalisar dokokin kasar za ta fadada hadin-gwiwa da majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, don sanya sabon kuzari ga ci gaban dangantakar kasashensu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China