in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta kyautata gidajen kula da tsoffin kasar
2018-02-02 11:06:06 cri
Kasar Sin ta samu nasarar warware matsaloli 200,000 da suka shafi al'amuran kula da tsoffi, bayan da kasar ta kammala binciken dukkan gidajen kula da tsoffin 41,700 dake kasar a shekarar da ta gabata, in ji mataimakin ministan kasar.

Gao Xiaobing, mataimakin minista mai kula da al'amuran walwalar jama'ar kasar, ya tabbatar da hakan a taron 'yan jaridu a birnin Beijing, fadar mulkin kasar, ya ce hukumomin gudanarwar kasar sun yi binciken dukkan gidajen kula da tsoffi wadanda aka yiwa rajista da wadanda ma ba'a yiwa rajistar ba.

Gao ya ce, a sakamakon hakan, matsalolin da gidajen kula da tsoffin kasar ke fuskanta ya yi matukar raguwa a rubu'in watanni ukun shekarar 2017 da ta gabata.

Kasar Sin tana samun karuwar adadin tsoffi. A halin yanzu, yawan mutanen da shekarunsu ya zarta 60 ya kai miliyan 241. Kana gidajen kula da tsoffi mallakar gwamnati ya yi karanci.

Mataimakin ministan ya ce, gwamnatin kasar za ta bullo da wani shiri na musamman wanda zai kara bunkasa ingancin gidajen kula da tsoffi, da kuma samar da wani tsari na kafa cibiyoyin kula da tsoffi karkashin tallafin al'umma ga tsoffin da suka fi sha'awar zama a cikin gidajensu, wanda ya dace da tsarin ka'idojin kula da tsoffi na kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China