in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gaza: UNRWA ta shiga yajin aiki don nuna adawa ga manufar Amurka ta takaita tallafi
2018-01-30 13:22:33 cri
A jiya ne reshen hukumar MDD dake ba da agaji ga 'yan gudun hijira Falasdinawa dake gabashin Asiya (UNRWA) a zirin Gaza ta fara wani yajin aiki, don nuna adawa da manufar kasar Amurka ta takaita tallafin da take baiwa hukumar.

A jiya ne dai, hukumar ta dakatar da aiki a makarantun da ta kafa a yankin Gaza, baya ga wasu wuraren jinya da su ma suka dakatar da aiki, in ban da hidima ga wadanda ke cikin mawuyacin hali. Ban da wannan kuma, daruruwan ma'aikatan hukumar sun bazu a kan tituna don gudanar da zanga-zanga.

Kafin wannan mataki, majalisar gudanarwar kasar Amurka ta sanar a ranar 16 ga wata cewa, za ta rage kudaden tallafin da yawansa ya kai dalar Amurka miliyan 65, wanda da ma ake da niyyar baiwa 'yan gudun hijira Falasdinawa ta hannun hukumar UNRWA. Ban da haka, majalisar ta kuma soke wani kudin tallafin na dalar Amurka miliyan 45 da aka yi shirin baiwa Falasdinu a shekarar 2018 da muke ciki.

Yadda kasar Amurka ta ke kokarin dakatar da tallafi ya shafi ayyukan hukumar agaji ta UNRWA matuka, saboda ba ta da kudin da take bukata na gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China