Kuma bisa hasashen da aka yi, shugaba Abdel Fattah Al-Sisi ne ake ganin zai iya lashe babban zaben da za a yi.
Tun a baya dai hukumar zaben kasar ta sanar da cewa, za a yi zaben shugaban kasar ta ranar 26 zuwa 28 ga watan Maris, idan babu wanda ya samu sama da rabin kuri'un da za a jefa a zagaye na farko na zaben, za a shirya zagaye na biyu na zaben.
Sa'an nan kuma, za a bayyana sakamakon zaben a ranar 1 ga watan Mayu. (Maryam)