in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya yi kira da a yaki da kalubalolin dake hana ci gaban Afirka
2018-01-29 09:21:42 cri

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya yi kira ga kasashen nahiyar Afirka da su tashi tsaye wajen yakar matsalar cin hanci dake zama Alla-kakai ga ci gaban nahiyar.

Shugaban ya yi wannan kiran ne jiya Lahadi yayin da yake jawabi a taron kolin kungiya tarayyar Afirka dake gudana a birnin Addis Ababan kasar Habasha. Ya kuma jaddada tasirin da matsalar cin hanci da satar kudade suke haifarwa ga harkokin jin dadin jama'a da tattalin arziki. A don haka ya bukaci kasashe mambobin kungiyar, da su yi kokarin samar da tsarin shugabanci da hukumomi na gari wajen ganin an kawar da matsalar cin hanci da ma abubuwan dake hana ci gaban nahiyar.

Kungiyar AU dai ta zabi shugaba Buhari a matsayin jagoran yaki da cin hanci da rashawa. Matsalar da Buharin ya ce ta lalata duk wani tsari na shugabanci.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China