in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na son ganin dankon zumuncin da ke tsakaninta da kasashen Larabawa ya kara haifar da sakamako mai kyau
2018-01-23 20:25:35 cri

Yau Talata a nan Beijing, Zhang Dejiang, shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin ya yi shawarwari da Meshal Faham M. Alsulami, shugaban majalisar kungiyar kawancen kasashen Larabawa, inda ya ce, ziyarar aiki da mista Alsulami yake yi a nan kasar Sin ita ce ta farko a tsakanin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin da majalisar kungiyar kawancen kasashen Larabawa, wadda take da muhimmiyar ma'ana wajen kyautata huldar da ke tsakanin Sin da kasashen Larabawa. Kasar Sin na son hada kai da kasashen Larabawa domin ganin dankon zumuncin da ke tsakaninsu ya kara haifar da sakamako mai kyau.

A nasa bangaren, mista Alsulami ya ce, kasashen Larabawa sun yaba muhimmiyar rawa da kasar Sin take takawa wajen wanzar da zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya, kana sun amince tare da goyon bayan shawarwari guda 4 da Sin ta gabatar dangane da warware batun Palesdinu. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China