in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar wakilan Sin sun halarci taron shekara-shekara na APPF
2018-01-21 13:26:03 cri
An yi taron shekara-shekara na dandalin tattaunawar majalisun dokokin yankin Asiya da Pacifik, watau APPF a birnin Hanoi na kasar Vietnam, daga ranar 18 zuwa ranar 20 ga watan nan da muke ciki.

Mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Chen Zhu, ya halarci taron a matsayin shugaban tawagar wakilan kasar Sin.

A yayin taron, Mr Chen, ya gabatar da jawabi inda ya bayyana cewa, a yayin cikakken zaman taron wakilan JKS karo na 19, kasar Sin ta bude wani sabon shafi na neman bunkasuwa. Kuma, tana son yin hadin gwiwa da kasashen dake yankin Asiya da Pacifik wajen kafa dangantakar abokantaka iri na nuna fahimtar juna da kuma neman ci gaba tare, ta yadda za a cimma moriyar juna, yayin gina wata makoma mai haske ga al'ummomin kasa da kasa.

Bugu da kari, a yayin taron, Chen Zhu, ya halarci taron ganawar babban sakataren kwamitin tsakiya na Jam'iyyar kwaminis ta kasar Vietnam Nguyen Phu Trong.

Sa'an nan, ya kuma gana da shugaban majalisar dokokin kasar Vietnam Nguyen Thi kim Ngan, da shugaban majalisar Hural na kasar Mongoliya Zandankhuu Enkhbold. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China