in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan za a kafa huldar kasa da kasa mai adalci
2018-01-19 19:17:51 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya yi martani ga furucin wasu jami'an kasashen Amurka, Japan da India, na cewar wai manufar kasar Sin game da yankin Indiya da tekun Pasific, da sauran yankunan teku, tana ta da hankali.

Lu Kang ya bayyana hakan ne a yau Jumma'a, a wani taron manema labaru da aka kira a birnin Beijing na kasar Sin. Ya ce a fannin tsarin al'amuran duniya, kasar Sin na fatan ganin an kafa wata sabuwar huldar kasa da kasa, irin ta girmamawa juna, da nuna adalci da daidaito, da neman yin hadin gwiwa don cimma nasarori tare. Wannan buri da kasar Sin ta sanya, a hakika ba zai zamo hanyar ta da hankalin wani ba, illa ma dai hanya ce ta wanzar da zaman lafiya, da bukatar ci gaban dukkan kasashen duniya.

Saboda haka jami'in ya bukaci kasashen da batun da shafa da su lura da kyakkyawar rawa mai ma'ana da kasar Sin take takawa a harkokin da suka shafi gamayyar kasa da kasa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China