in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Gabon suna son kara musayar ra'ayi ta fuskar harkokin majalissar dokoki
2018-01-17 20:06:45 cri
Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Zhang Dejiang, ya gana da shugabar majalissar dattawan kasar Gabon Madam Lucie Milebou a yau Laraba, a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

A wajen ganawar, mista Zhang Dejiang, ya ce majalissar wakilan jama'ar kasar Sin tana dora muhimmanci kan kokarin raya huldar dake tsakaninta da majalissun kasar Gabon wato na dattawa da na wakilai, sa'an nan tana son kara musayar ra'ayi tare da bangaren Gabon kan al'amuran kafa dokoki, da sa ido kan yadda ake bin dokokin, gami da aikin gudanar da mulki.

A nata bangaren, madam Milebou ta ce, bangaren Gabon na son karfafa hadin gwiwa tare da kasar ta Sin, don kara kyautata huldar dake tsakaninsu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China