in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ribar da kamfanoni mallakar gwamnatin kasar Sin suka ci ta zarce kudin Sin yuan biliyan 1400 a bara
2018-01-17 11:41:43 cri
Shen Ying, jami'a a hukumar dake kula da kadarorin gwamnati ta majalisar gudanarwa ta kasar Sin ta bayyana a nan birnin Beijing cewa, a shekarar 2017 da ta gabata, kamfanoni 98 mallakar gwamnati sun samu ribar da ta zarce kudin Sin yuan biliyan 1400, alkaluman da suka wuce yadda aka yi hasashe.

Shen Ying ta bayyana a yayin taron manema labarai da majalisar gudanarwar kasar ta kira a jiya, cewar kamfanonin sadarwa mallakar gwamnati sun kara inganta harkokinsu na sadarwa tare kuma da rage kudin da ake biya, a yayin da kamfanonin sarrafa man fetur da na samar da wutar lantarki suka yi kokarin tsimin makamashi tare kuma da rage hayakin da suke fitarwa, matakin da ya kai su ga rage kudi kimanin yuan biliyan 200. Har wa yau, sun kuma taimaka ga saukaka fatara a kasar, inda suka zuba jarin da ya kai kimanin yuan biliyan 20. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China