Yayin da yake gabatar da jawabi a wajen bikin bude taron gaggawa na kwamitin tsakiya na kungiyar PLO a birnin na Ramallah, Abbas ya ce, ba zai yarda Amurka ta nuna mulkin danniya ba. A cewarsa, za su yi la'akari da hanyoyi daban-daban da za su bi wajen daidaita rikicin bangarorin biyu, amma Amurka ba ta ciki.
Abbas ya kuma ce, Palestinu za ta ci gaba da tuntubar masu son shimfida zaman lafiya na Isra'ila, a wani kokari na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin bangarorin biyu.(Murtala Zhang)