in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Isra'ila sun lalata wata hanyar karkashin kasa a kudancin yankin Gaza
2018-01-15 11:57:58 cri
Sojojin tsaron kasar Isra'ila sun ce, da sanyin safiyar jiya Lahadi ne, suka lalata wata hanyar dake karkashin kasa, wadda ta hada kudancin yankin Gaza da Isra'ila, kana ta shiga cikin kasar Masar.

Mai magana da yawun rundunar sojan tsaron kasar Isra'ila ya ce, kungiyar Hamas ce ta tona wannan hanyar karkashin kasa, wadda ke kasan bututun jigilar iskar gas da man dizal wanda ya hada Isra'ila da yankin Gaza, kana tana karkashin wata tashar bincike ta rundunar sojan tsaron Isra'ila.

Rahotanni na cewa, sojojin Isra'ila sun dauki matakan soja na lalata wannan hanya ne a wani wuri mai suna Kerem Shalom dake kan iyakokin Isra'ila da Gaza.

A wannan rana, sojojin Isra'ila sun rufe yankin cinikayya na Kerem Shalom iyakarta da Gaza, wannan shi ne karo na biyu da sojojin Isra'ila suka rufe wannan muhimmin wurin cinikayya a cikin wata guda. A cewar rundunar sojan tsaron Isra'ila, kamata ya yi kungiyar Hamas ta dauki alhakin hakan.

Wannan hanya ita ce hanyar karkashin kasa ta uku ta Palesdinu da sojojin Isra'ila suka lalata a cikin watanni biyu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China