in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta kwatanta kalaman Trump kan wasu 'yan cin rani a matsayin abin kunya kuma na nuna wariyar launin fata
2018-01-12 20:50:44 cri
Ofishin babban kwamishinan kula da kare hakkin bil-Adama na MDD ya bayyana cewa, kalaman da shugaban Amurka Donald Trump ya yi a kan 'yan cin rani daga kasashen Haiti da Afirka abin kaduwa ne, abin kunya kuma kalamai ne na nuna wariyar launin fata.

An ruwaito Trump yayin zaman MDD, a lokacin da yake tambaya a ranar Alhamis dalilin da ya sa Amurka za ta karbi Karin 'yan cin rani daga kasashen Haiti da wulakantattun kasashe a Afirka, maimakon kasashe kamar Norway. Rahotanni na cewa, Trump dai ya yi watsi da dokar shigi da fice da manyan jam'iyyun siyasu a majalisar dokokin kasar suka gabatar masa.

Mai magana da yawun UNHCHR Rubert Colville ya ce, kalaman shugaban abin kaduwa ne kuma abin kunya. Kalmar da ta dace a yi amfani da ita, ita ce nuna wariyar launin fata. Don haka bai kamata shugaban ya kira kasashen da ma nahiyar da baki dayan al'ummunsu ba fara ne ba a matsayin wulakantattu ba. A saboda haka ba za a lamunci haka ba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China