in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Netanyahu: A soke hukumar agazawa 'yan gudun hijira Palasdinawa
2018-01-08 10:48:38 cri
Bayan da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi barazanar dakatar da samar da tallafi ga bangaren Palasdinu, a nashi bangaren, firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya furta a jiya Lahadi cewa, ya kamata a soke hukumar kai dauki ga 'yan gudun hijirar Palasdinawa ta MDD (UNRWA).

Mista Netanyahu ya yi furucin ne a wajen wani taron da majalisar ministocin kasar Isra'ila ke gudanarwa a ran nan, inda ya ce hukumar da MDD ta kafa don kula da 'yan gudun hijirar Palasdinawa, a hakika ita ce dalilin da ya sa aka dade ana fama da matsalar 'yan gudun hijirar Palasdinawa.

Ban da haka kuma, ya bukaci a mika ikon hukumar na kula da asusun tallafawa 'yan gudun hijirar Palasdinawa ga ofishin babban kwamishina mai kula da batun 'yan gudun hijira na MDD.

A ranar 2 ga watan da muke ciki ne, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya rubuta a shafin sa na sada zumunta na Twitter cewa, zai dakatar da agajin da ake baiwa Palasdinu. A cewarsa, kasar Amurka ta kan baiwa Palasdinu dala fiye da miliyan 100 a ko wace shekara, amma duk da haka ba ta samu godiya ko kuma girmamawa daga bangaren Palasdinu ba, ganin yadda Palasdinu ta ki yin shawarwari tare da Isra'ila, game da yiwuwar kulla wata yarjejeniyar sulhu a tsakaninsu, in ji shugaban.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China