A kokarin kara tsaurara matakan kiyaye da kula da tabkuna, kasar Sin za ta bullo da matakan kula da tabkunan da ke kasar baki daya kafin karshen shekarar 2018. Tsarin zai bukaci jami'ai a matakai daban daban da su sauke nauyin dake wuyansu na kiyaye da kula da tabkunan da ke wuraren aikinsu.
Mataimakin ministan kula da albarkatun ruwa na kasar Sin Zhou Xuewen wanda ya bayyana hakan a Jumma'ar nan, ya ce idan aka gano an lalata muhallin tabkuna, babu shakka sai an nemo wanda ya aika wannan laifi ko da ba ya kan mukaminsa.