in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci 'yan Afrika su yaki cin hanci kamar yadda yake kunshe cikin ajandar taron AU
2018-01-05 11:05:49 cri
Yayin da Tarayyar Afrika AU ta bayyana yaki da cin hanci a matsayin abun da zai mamaye babban taronta dake karatowa, kwararru da masana sun jadadda muhimmanci dake akwai na yaki da cin hanci da rashin kyakkyawan shugabanci domin ci gaban nahiyar.

A baya-bayan nan ne tarayyar ta sanar da cewa, za ta gudanar da taron gama gari na shugabannin kasashe da Gwamnatocin Afrika karo na 30, daga ranar 22 zuwa 29 ga wannan wata a hedkwatarta dake Addis Ababa babban birnin Habasha.

Taron da aka yi wa taken 'nasarar yaki da cin hanci: hanya mafi dorewa ta sauya nahiyar Afrika', ya ja hankalin masana da kwararru saboda tasirin da zai yi ga ci gaban nahiyar baki daya.

A jawabinsa na sabuwar shekara, shugaban hukumar kula da ayyukan AU Moussa Faki Mahamat, ya ce yaki da cin hanci shi ne jigon ci gaban nahiyar da kawar da bambamci a tsakanin al'ummarta.

A cewarsa, cin hanci ya haifar da rashin daidaito tsakanin al'ummomin tare da keta dokoki a nahiyar, ya na mai cewa duk da shaidu sun nuna cewa cikin shekaru 5 da suka gabata, nahiyar ta dauki matakai masu karfafa gwiwa, har yanzu da sauran rina a kaba.

Har ila yau, Moussa Faki Mahamat ya ce a kokarin magance manyan kalubalen da cin hanci ya haifar a nahiyar, zauren tarayya ya ayyana shekarar 2018 a matsayin shekarar yaki da cin hanci ta nahiyar Afrika mai taken 'nasarar yaki da cin hanci: hanya mafi dorewa ta sauya nahiyar Afrika'. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China