in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
PLO tace kuri'ar da majalisar Knesset ta Israeli ta kada ta hade birnin Kudus ta biyo bayan matakin da Trump ya dauka ne
2018-01-03 13:41:57 cri
Sakatare janar na kwamitin zartaswa na kungiyar fafutukar 'yantar da alummar Palastinawa PLO, Saeb Erekat, ya bayyana cewa, kuri'ar da majalisar dokokin Israeli Knesset ta kada game da dokar hada birnin Kudus ta biyo bayan matakin da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauka ne.

Cikin jawabin da ya gabatar ta gidan radiyon Palastinu, Erekat yace, kuri'ar da majalisar Israeli Knesset ta kada, da kuma matakin da jami'yyar Likud ta dauka na kwace ikon yamma da kogin Jordan sakamako ne na matakin da Trump ya dauka na ayyana Kudus a matsayin babban birnin Isra'ila a ranar 6 ga watan Disambar shekarar bara.

Erekat ya fada cewa, wannan yana daya daga cikin sabuwar dangantakar hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra'ila na yin mulkin kama-karya da kuma lalata manufofin wanzar da zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu, ya kara da cewa, shugaban Palastinawa Mahmoud Abbas, ya ayyana wasu dabarun da Palastinawa zasu yi amfani dasu wajen tunkarar wannan al'amari don magance matsalar Palastinawan.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China