in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin tsakiya da kwamitin gudanarwar sojoji na kasar Sin za su tafiyar da harkokin rundunar 'yan sanda masu dauke da makamai
2017-12-28 10:45:22 cri
Daga ranar 1 ga watan Janairun shekarar 2018, rundunar jami'an 'yan sanda masu dauke da makamai za su koma karkashin gudanarwar jamiyyar kwaminis ta kasar Sin CPC, da kwamitin tsakiya mai kula da harkokin sojojin kasar Sin CMC, kamar yadda kwamitin tsakiya na jamiyyar CPC ya sanar a ranar Laraba.

Kamar yadda sanarwar ta nuna, hukumar rundunar 'yan sanda masu dauke da makamai za ta kasance a matsayin wani sashe ne karkashin ikon CMC, kuma ba za ta ci gaba da kasancewa a karkashin gudanarwar majalisar koli ta kasar Sin ba.

Sanarwar ta ce, za'a kafa wani tsarin gudanarwa na hadin gwiwa tsakanin kwamitin tsakiya, da hukumomin gudanarwa na kananan yankuna da kuma jami'an 'yan sanda masu dauke da makamai.

Kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin ya bukaci gwamnatoci a dukkan matakai, da rundunar sojoji ta PLA, da kuma jami'an 'yan sanda masu dauke da makamai da su aiwatar da wannan sabon tsari domin tafiyar da al'amurran tsaron kasa yadda ya kamata. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China