Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa, ya nada tsaffin kwamandojin da suka taka rawa a rundunar tsaro da wanzar da zaman lafiya ta mayakan kasar Constantino Chiwenga, da Kembo Mohadi a matsayin mataimakan sa biyu.
Wata sanarwa da aka fitar ta bayyana cewa, nadin da shugaban ya yi wa jami'an biyu, da rantsuwar kama aiki da za su yi a Alhamis din nan, sun dace da tanajin kundin mulkin kasar.
Hakan dai na zuwa ne bayan da a baya aka nada mutanen biyu a matsayin sakatarori a jam'iyyar Zanu-PF mai mulkin kasar.(Saminu)