Cikin sanarwar, kakakin fadar shugaban falastinawan Nabil Abu Rudeineh, ya bayyana cewa, kudurin da aka zartas a zauren MDD ya nuna goyon bayan da gamayyar kasa da kasa suka nunawa al'ummar Falastinawa wajen kare ikonsu, kana ya kuma nuna goyon bayan da dokar kasa da kasa ta yiwa Falesdinu.
Haka kuma ya kara da cewa, bisa dokar kasa da kasa, birnin Kudus ya kasance yanki ne da aka mamaye, kuma ba wanda zai iya yin tababa kan wannan batu. (Maryam)